Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Kotu Ta Yanke wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Kan Hallaka Ango a Kano

      March 4, 2026

      Mutane 2 Sun Mutu, 8 Sun Jikkata a Harin Boko Haram a Yobe

      March 4, 2026

      ADC Ta Nuna Goyon Bayanta Ga El-Rufai Da Malami

      March 4, 2026

      Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Man Fetur

      March 3, 2026

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026
    • Siyasa

      ADC Ta Nuna Goyon Bayanta Ga El-Rufai Da Malami

      March 4, 2026

      Doguwa Ya Yi Murabus Daga Muƙamin Kwamishinan Ruwa Na Kano

      March 3, 2026

      Gwamnan Adamawa Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

      February 27, 2026

      NDLEA Ta Kama Wata Mata Mai Cikin Bogi Ɗauke da Hodar Iblis a Iyakar Seme

      February 22, 2026

      Jam’iyyun Adawa Sun Kaurace wa Zaɓen Kano, APC Ta Lashe Kujerun Majalisa a Rivers

      February 22, 2026
    • Addini

      Bauchi Ta neman ƙarin Kujerun Hajji Daga Saudiyya

      February 16, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Umarci Ƴan Najeriya Su Fara Duban Jinjirin Watan Ramadan Ranar Talata

      February 16, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Ambasada Ismail Abba Yusuf a Matsayin Sabon Shugaban NAHCON

      February 11, 2026

      Sheikh Usman Kusfa Zaria (Rigi-rigi) Ya Rasu

      February 2, 2026

      Jigawa Ta Fara Gwajin Lafiya ga Maniyyatan Hajjin 2026

      January 28, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ba a Fasa Bututun Mai Ko Ɗaya a Niger Delta a 2025 Ba – Sojoj

      January 20, 2026

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Hukumar Kwastam Ta Gargadi Masu Neman Aiki a Hukumar Da Su Guji Labaran Ƙarya Da Ake Yaɗawa
    Featured

    Hukumar Kwastam Ta Gargadi Masu Neman Aiki a Hukumar Da Su Guji Labaran Ƙarya Da Ake Yaɗawa

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Hukumar Kwastam ta Nijeriya (NCS) ta yi gargaɗi ga masu neman aiki a hukumar a zangon daukar ma’aikata na 2025 da su yi watsi da wasu sakonninbda su ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin nuna jerin sunayen wadanda aka zaɓa daga kowace jiha domin tantancewa. Hukumar ta bayyana irin wannan bayanin a matsayin ƙarya kuma ba shi da tushe. A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin X a ranar Asabar mai taken “Unverified Social Media Post on 2025 Nigeria Customs Service Recruitment Exercise,” hukumar ta ce sakon bai fito daga gare ta ba ko daga kowane kafar sadarwa na hukuma.

    Hukumar ta jaddada cewa tsarin tantancewa zai kasance cikin gaskiya da adalci, bisa cancanta, kuma cikin ka’idojin da suka dace da na duniya. Ta kuma tunatar da jama’a cewa duk wani muhimmin bayani game da daukar ma’aikata ana sanar da shi ne kai tsaye ga wadanda suka shiga jerin masu cin gajiyar tsarin, ta hanyar shafi na musamman na sabunta bayanai: https://updates.customs.gov.ng. Hukumar ta bayyana cewa daukar ma’aikatan da ta fara a ranar 27 ga Disamba, 2024 ya jawo aikace-aikace 573,523 daga rukunan Superintendent, Inspectorate da Customs Assistant. Daga cikin su, mutum 286,697 ne suka tsallake matakin tantance takardu kuma aka gayyace su zuwa jarrabawar kwamfuta (CBT) ta farko, wadda aka gudanar a matakai domin tabbatar da adalci da inganci.

    Bayan kammala wannan matakin na farko, an bayyana cewa dukkan rukunin sun shiga CBT, amma wadanda suka yi nasara a rukunin Superintendent kadai aka gayyata zuwa mataki na biyu. Wannan mataki ya gudana ne a cibiyoyi da aka ware a shiyyoyi shida na ƙasar kamar yadda aka sanar tun farko. Hukumar ta kuma jaddada cewa tana bin tsarin “Federal Character” domin tabbatar da daidaito a daukar ma’aikata daga dukkan yankuna.

    Hukumar Kwastam
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleTinubu Bai Damu Da Halin Da Ƴan Najeriya Su Ke Ciki Ba – Dino Melaye
    Next Article Gwamnatin Tarayya Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 106 Allurar Rigakafi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Kotu Ta Yanke wa Mutane Biyu Hukuncin Kisa Kan Hallaka Ango a Kano

    March 4, 2026
    Featured

    Mutane 2 Sun Mutu, 8 Sun Jikkata a Harin Boko Haram a Yobe

    March 4, 2026
    Featured

    ADC Ta Nuna Goyon Bayanta Ga El-Rufai Da Malami

    March 4, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202544 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202527 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.