Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Kotu Ta Sake Dakatar Da Babban Taron PDP

      November 11, 2025

      Bayan 2026 Bazan Sake Buga Gasar Kofin Duniya Ba – Ronaldo

      November 11, 2025

      Masu Zanga-zanga Sun Isa Majalisar Dokoki Dan Neman Tabbatar Da Ramat a Matsayin Shugaban NERC

      November 11, 2025

      Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO

      November 11, 2025

      EFCC Na Neman Tsohon Gwamnan Bayelsa Ruwa-a-Jallo

      November 11, 2025
    • Siyasa

      Kotu Ta Sake Dakatar Da Babban Taron PDP

      November 11, 2025

      INEC Ta Ayyana Soludo a Matsayin Wanda Ya Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

      November 9, 2025

      An Rantsar Da Shugaban Ƙasa Mafi Tsufa a Duniya

      November 7, 2025

      Gombe Na Amfana Da Cire Tallafin Man Fetur – Inuwa Yahya

      November 4, 2025

      Sabon Rikici Na Shirin Kunno Kai Tsakanin Sanata Natasha Da Akpabio

      November 4, 2025
    • Addini

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025

      Ƙungiyoyin Fityanul Islam Da Samarin Tijjaniyya Sun Yi Ƙarar Gwamnatin Kano a Kotu

      November 5, 2025

      Saudiyya Ta Ragewa Najeriya Kujerun Hajjin 2026

      October 17, 2025

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci a Samar Da Dokokin Amfani Da Kafafen Sada Zumunta a Najeriya

      October 16, 2025

      Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Laifin Yin Aure Ba Tare Da Amincewar Iyayensu Ba

      October 13, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Masu Zanga-zanga Sun Isa Majalisar Dokoki Dan Neman Tabbatar Da Ramat a Matsayin Shugaban NERC
    Featured

    Masu Zanga-zanga Sun Isa Majalisar Dokoki Dan Neman Tabbatar Da Ramat a Matsayin Shugaban NERC

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Wasu masu zanga-zanga sun mamaye ginin Majalisar Dokoki ta tarayya a Abuja, domin nuna damuwarsu kan jinkirin tabbatar da nadin Injiniya Abdullahi Ramat a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Lantarki ta Kasa (NERC), wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya mika sunansa zuwa Majalisar watanni da suka gabata. Masu zanga-zangar, da suka hada da kungiyoyin fararen hula da magoya bayan Ramat, sun rera wakokin hadin kai dauke da kwalaye da ke kira ga Majalisar da ta kammala tabbatar da nadin cikin gaggawa.

    A cewar jagoran masu zanga-zangar, Ahmed Suleiman, Ramat ya riga ya sami amincewa daga kwamitin Majalisar da ta duba cancantarsa, amma an dakatar da nadin nasa saboda wasu “masu ruwa da tsaki” da ke kokarin hana shi shiga ofis. Ya ce akwai masu amfani da siyasa wajen yada bayanan karya domin hana shi samun wannan mukami, duk da cewa yana da gogewa da kwarewar da ake bukata a bangaren wutar lantarki.

    Sai dai Majalisar Dattawa ta yi watsi da zargin cin hanci da ake cewa wasu sanatoci sun ci dala miliyan 10 domin hana tabbatar da nadin Ramat. Kakakin Majalisar, Yemi Adaramodu, ya ce an dai dakatar da nadin ne saboda wasu koke-koke da aka samu daga jama’a da kuma cikin gida. Ya jaddada cewa Majalisar ba za ta yi gaggawa wajen tabbatar da kowane nade-nade ba idan har akwai abin da ke bukatar karin bincike.

    Nadin Ramat dai na ci gaba da jawo cece-kuce a lokacin da kasar ke fuskantar karin farashin wutar lantarki da karancin isasshen wuta. Yanzu ana jiran ci gaba daga bangaren Majalisar Dattawa, wadda ta ce za ta cigaba da nazari kafin daukar matakin karshe.

    NERC
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleMutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO
    Next Article Bayan 2026 Bazan Sake Buga Gasar Kofin Duniya Ba – Ronaldo
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Kotu Ta Sake Dakatar Da Babban Taron PDP

    November 11, 2025
    Featured

    Bayan 2026 Bazan Sake Buga Gasar Kofin Duniya Ba – Ronaldo

    November 11, 2025
    Featured

    Mutane Miliyan 24 Na Fama Da Ciwon Suga a Afrika – WHO

    November 11, 2025
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202537 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202536 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202526 Views

    Matuƙar Ba’a Yi Yadda Aka Yi a Afghanistan Ba Baza’a Kawo Ƙarshen Ta’addanci a Najeriya Ba – Amurka

    November 6, 202522 Views

    Zama a Banɗaki Fiye Da Kima Kan Haifar Da Matsala Ga Lafiyar Ɗan Adam – Likita

    October 28, 202520 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2025 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.