Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Matuƙar Ba’a Yi Yadda Aka Yi a Afghanistan Ba Baza’a Kawo Ƙarshen Ta’addanci a Najeriya Ba – Amurka
    Featured

    Matuƙar Ba’a Yi Yadda Aka Yi a Afghanistan Ba Baza’a Kawo Ƙarshen Ta’addanci a Najeriya Ba – Amurka

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 6, 2025No Comments2 Mins Read

    An rawaito cewa rundunar sojin Amurka ta tsara yiwuwar kai hare-haren sama a Najeriya sakamakon umarnin da Shugaba Donald Trump ya bai wa Ma’aikatar Tsaron ƙasar, domin kare Kiristoci daga hare-haren ta’addanci. Rahoton jaridar New York Times ya ce an gabatar da zaɓuɓɓuka uku ga ma’aikatar tsaro: na “mai nauyi”, wanda zai haɗa da tura jiragen yaki da tawagar jirgin ruwa a Gabar Tekun Guinea; na “matsakaici” da ke amfani da jiragen yaki marasa matuki wajen kai hare-haren cibiyoyin ‘yan ta’adda; da na “mai sauƙi” da ke takaita kai tsaye ga musayar bayanan tsaro da tallafin leƙen asiri.

    Sai dai jami’an soja a Pentagon sun ce ko da Amurka ta kai hare-haren sama, hakan ba zai kawo ƙarshen matsalolin tsaro a Najeriya ba muddin ba a tsaya kan faɗa mai zurfi kamar yadda aka yi a Afghanistan ko Iraq, wanda a cewar rahoton babu wanda ke goyon bayansa a Washington a yanzu. A baya dai Trump ya yi barazanar tura sojojin Amurka Najeriya domin dakatar da abin da ya kira “kisan gilla ga Kiristoci”, lamarin da gwamnatin Najeriya ta musanta tana mai cewa matsalar ba ta addini bace, illa matsalar ta’addanci da ta shafi kabilu da al’ummomi da dama.

    A gefe guda, kasar China ta nuna goyon bayanta ga Najeriya, tana mai cewa ba ta amince da kowacce ƙasa ta shiga harkokin cikin gida na wata ƙasa karkashin sunan kare addini ko ‘yancin dan Adam ba. Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen China, Mao Ning, ta ce kasar na goyon bayan ‘yancin Najeriya da bin hanyoyin diflomasiyya wajen magance matsalolin tsaro.

    Gwamnatin Najeriya ta nanata cewa tun daga shekarar 2023 ana samun ci gaba wajen yaki da ta’addanci, inda ta ce an hallaka sama da mayaka 13,500 tare da ceto mutane fiye da 11,000 da aka yi garkuwa da su. Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya bayyana cewa gwamnati na kare ‘yan ƙasa ba tare da bambancin addini ba, tana kuma maraba da haɗin gwiwa da Amurka matuƙar an mutunta ikon Najeriya a kan yankinta.

    Amurka
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleShekarau @ 70: Damuwa Bata Taɓa Hanani Bacci Ba – Shekarau
    Next Article Gidaje 20 Da Ake Zargina a Kansu Ba Nawa Bane Ne Waɗanda Mahaifinmu Ya Bar Mana Gado Ne – Abba Kyari
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.