Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 17 a Kaduna da Filato
    Featured

    Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 17 a Kaduna da Filato

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 2, 2025No Comments2 Mins Read

    A kalla mutum 17 ne suka rasa rayukansu a hare-hare daban-daban da ‘yan bindiga suka kai a jihohin Kaduna da Filato a ƙarshen mako. A Kaduna, ‘yan bindigar sun kutsa cikin garin Damakasuwa da ke cikin masarautar Chawai, ƙaramar hukumar Kauru, inda suka kashe mutum bakwai da jikkata wani. Shaidun gani da ido sun ce maharan sun zo da yamma, suka fara harbe-harbe ba gaira ba dalili, lamarin da ya sa mazauna yankin suka gudu cikin daji domin tsira da rayukansu.

    Mai martaba sarkin Chawai, Alhaji Yahaya Muhammad, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an kashe mutane biyar a wurin, yayin da wasu biyu suka mutu daga baya saboda munanan raunuka. Ya ce an sake samun natsuwa bayan isowar jami’an tsaro, tare da kira ga jama’a da su kwantar da hankali. Wani matashin yankin, Barnabas Chawai, ya ce maharan sun far wa jama’a ne a lokacin da wasu ke bacci, wasu kuma har yanzu suna harkokinsu na yamma.

    A jihar Filato kuwa, an tabbatar da mutuwar mutum goma a hare-hare guda biyu da suka faru tsakanin Juma’a da Asabar. A cewar wani jagoran al’umma, Rwang Tengwon, maharan da ake zargin Fulani makiyaya ne sun kai farmaki a garin Kwi, ƙaramar hukumar Riyom, inda suka kashe mutum bakwai. Haka kuma an kashe mutum uku a garin Pushit, ƙaramar hukumar Mangu, kamar yadda ƙungiyar ci gaban Mwaghavul ta tabbatar a wata sanarwa.

    Hukumomin ‘yan sanda a jihohin biyu ba su fitar da cikakken bayani ba har zuwa lokacin da aka wallafa rahoton. Sai dai gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya tabbatar da matakan tsaro da suka haɗa da hana kiwon dare da jigilar shanu bayan ƙarfe 7 na yamma da kuma hana amfani da babura daga 7 na yamma zuwa 6 na safe, domin rage hare-haren da ke addabar jihar.

    Kaduna
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleHar Yanzu Bamu Janye Dakatarwar Shekaru 30 Da Mu Ka Yi Wa El-Rufai Ba – SDP
    Next Article Ƴan Sanda Sun Kama Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Shanu a Jigawa
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.