Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Mata 8 a Tsanyawa
    Featured

    Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Mata 8 a Tsanyawa

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 25, 2025No Comments2 Mins Read

    An cika da fargaba a daren Litinin 25 ga Nuwamba 2025, tsakanin ƙarfe 11 na dare zuwa 12 na tsakar dare, lokacin da ‘yan bindiga suka afka ƙauyen Biresawa da ke ƙaramar hukumar Tsanyawa a jihar Kano suka kuma yi garkuwa da mutane akalla takwas. Maza biyu da mata shida ne aka tabbatar da sacewa, inda al’ummar yankin suka ce ba a samu labarin inda aka tafi da su ba har yanzu. Shaidu sun bayyana cewa maharan sun shigo ƙauyen ne a ƙafa, dauke da bindigogi, tare da yin barazana ga mazauna wurin.

    Wasu mazauna sun ce an shaida motsin barayin tun kafin kai farmakin, inda aka sanar da jami’an tsaro amma ba a samu dakatar da su ba. A Yankibi, Sarmawa da Gano – dukkansu a cikin Tsanyawa – maharan da ake kiyasta fiye da 50, dauke da babura, sun yi harbe-harbe tare da sace mutane fiye da goma, yawanci mata. Kakakin al’umma, Kabiru Usman, ya ce matarsa, diyarsa mai shekara 17, da matan ‘yan uwansa na cikin wadanda aka tafi da su.

    Rahotanni sun nuna cewa mazauna yankin da jami’an sa-kai sun yi ƙoƙarin bin sawun maharan, amma suka gaza gano inda suka nufa bayan sun tsallaka zuwa jihar Katsina. Yayin da hare-haren baya-bayan nan ke ci gaba a Shanono da Bagwai, al’ummomi da dama na tserewa gidajensu, wasu na kwana a jeji ko ƙauyuka daban don gujewa kama su da daddare. Wasu mazauna sun bayyana cewa tsoro da damuwa sun yi katutu, musamman ma saboda hare-haren da suka saba a yankin da suka hada da sace mata biyar a Yan Kwada makonni kadan da suka gabata.

    Yayin da ake ci gaba da neman bayani, Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, bai amsa kiran manema labarai ba har zuwa lokacin kammala rahoton. Al’ummar yankin na roƙon gwamnati da hukumomin tsaro da su ɗauki matakai na gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi, tare da dawo da mutanen da aka sace cikin gaggawa.

    Tsanyawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGanduje Zai Kafa Hukumar Hisbah Mai Zaman Kanta a Kano
    Next Article Da Ɗumi-ɗumi : An Ceto Ɗalibai Mata 24 Da Aka Sace a Kebbi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.