Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ganduje Zai Kafa Hukumar Hisbah Mai Zaman Kanta a Kano
    Featured

    Ganduje Zai Kafa Hukumar Hisbah Mai Zaman Kanta a Kano

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 25, 2025No Comments2 Mins Read

    Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana shirin kafa wata sabuwar rundunar sa-kai makamanciyar Hisbah karkashin Ganduje Foundation, domin ɗaukar tsofaffin jami’ai 12,000 da gwamnatin jihar ta sallama. Ganduje, wanda ya kasance tsohon shugaban APC na ƙasa, ya ce korar jami’an ta kasance rashin adalci, inda aka gabatar masa da rahoton tantance su daga kwamitin Dr. Baffa Babba Dan-Agundi.

    Rahoton ya tabbatar da sunaye da bayanan tuntuɓar waɗanda aka kora, tare da bayyana cewa za su kasance tare da Ganduje a sabon tsarin. Ganduje ya ce rundunar za ta yi aiki ne ba a matsayin hukuma ta gwamnati ba, sannan za ta kasance mai zaman kanta da sunan Independent Hisbah, tare da yiwuwar ɗaukar ƙarin masu son shiga daga cikin al’umma.

    Manyan jiga-jigan APC sun halarci taron, ciki har da Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, Murtala Sule Garo, Abdullahi Abbas da Rabiu Sulaiman Bichi. An kuma bayyana cewa tsohon kwamandan Hisbah, Sheikh Muhammad Harun Ibn Sina, shi ne ake sa ran zai jagoranci sabuwar rundunar, wadda aka ce za ta yi ayyukan wa’azi, taimako, bayar da agajin gaggawa da “hankyatar da alheri da hani ga mummuna.”

    Ibn Sina ya ce rundunar — wadda za ta kasance da suna Khairun Nas — ba zata yi takarar hukuma ba, kuma ba lallai ta biya albashi ba, sai dai tana iya samun tallafi daga mutane ko ƙungiyoyi domin biyan ɗan kuɗin alawus. Ya kara da cewa shirin bai kammala kafuwa ba tukuna, amma zai kasance a buɗe ga kowa da kowa ba wai ga waɗanda aka sallama kaɗai ba.

     

    Hisbah
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleMatsalar Tsaro: Abin Kunya Ne Yadda Ake Rufe Makarantu a Najeriya – Buba Galadima
    Next Article Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Mata 8 a Tsanyawa
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202543 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.