Gwamnatin Tarayya ta ce kusan kashi 60 cikin 100 na masu amfani da wutar lantarki a Najeriya yanzu suna da mita, yayin da ake ƙoƙarin rage gibin mita da kuma kawo ƙarshen ƙiyasin kuɗin wutar lantarki.
Daraktan-Janar na Ofishin Kamfanonin Gwamnati (BPE), Ayodeji Ariyo Gbeleyi, ya ce an riga an sanya mita 668,000 daga cikin mita 1,033,000 da aka samar ƙarƙashin shirin da Bankin Duniya ke ɗaukar nauyinsa da dala miliyan 500.
Ya bayyana hakan ne yayin taron Majalisar Kula da Kamfanoni (NCP) na biyu a shekarar 2026, wanda Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya jagoranta a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja. Gwamnatin ta ce shirin na da nufin rage gibin mita da kuma kawo ƙarshen ƙiyasin kuɗin wutar lantarki.
Gbeleyi ya kuma ce jihohi kusan 17 sun kafa hukumomin da za su kula da harkokin wutar lantarki tun daga watan Afrilu 2024. Ya ƙara da cewa an umarci hukumomin da abin ya shafa su tattauna kan gyare-gyaren da suka dace ga Dokar Wutar Lantarki domin daidaita aiwatar da ita.
