Kotun Daukaka Kara da ke Abuja ta bayar da umarnin dakatar da aiwatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ya umarci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta soke rajistar jam’iyyar ADC da wasu jam’iyyu hudu.
Kotun ta umarci INEC da kada ta dauki wani mataki kan soke rajistar jam’iyyun har sai an kammala sauraron karar da jam’iyyun da abin ya shafa suka shigar. Wannan mataki ya dakatar da aiwatar da hukuncin da aka yanke a baya.
A ranar Litinin ne Mai Shari’a Peter Lifu na Babbar Kotun Tarayya ya umarci a soke rajistar ADC, Accord Party da wasu jam’iyyu uku bisa zargin rashin cika wasu sharuddan doka. Sai dai kwamitin alkalai uku na Kotun Daukaka Kara ya soki matakin, yana mai cewa an yi watsi da umarnin babbar kotu da ke sama.

