Majalisar Wakilai ta gayyaci Ministan Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki tare da Darakta Janar na Ofishin Kasafi domin su yi bayani kan yadda aka sanya kasafin Naira biliyan 1.3 na Hukumar PFIPC cikin kasafin kudin 2026. Hakan ya biyo bayan amincewa da kudirin gaggawa da Hon. Yusuf Gagdi ya gabatar.

Majalisar ta kuma kafa kwamitin wucin gadi domin binciken yadda aka shigar da kasafin kungiyar cikin tsarin kasafin kudin, tare da umartar a tantance dukkan hukumomin da ke cikin kasafin 2025 da 2026. Haka kuma ta bukaci kada a fitar da wani kudi ga PFIPC har sai an kammala bincike.

A bangare guda, Majalisar Dattawa ta ki amincewa da gudanar da nata binciken, tana mai cewa ta jira sakamakon binciken da Shugaba Bola Tinubu ya umurci ICPC ta gudanar. Shi kuwa tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya bukaci a kafa kwamitin bincike mai zaman kansa domin gano gaskiyar lamarin.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version