Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » PDP Zata Wargaje Matuƙar Aka Daina Shawara Da Ni – Wike
    Featured

    PDP Zata Wargaje Matuƙar Aka Daina Shawara Da Ni – Wike

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 25, 2025No Comments2 Mins Read

    Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya yi gargaɗin cewa jam’iyyar PDP za ta lalace idan gwamnoninta suka ci gaba da watsi da shi daga muhimman shawarwarin jam’iyyar. Yayin wata tattaunawa da manema labarai a Abuja, Wike ya bayyana takaicinsa kan yadda ake ware shi daga tattaunawa da yanke shawara, duk da irin rawar da ya taka wajen gina jam’iyyar.

    Wike ya ce ba wai jam’iyyar APC bace ke haddasa matsalolin PDP ba, illa dai kuskuren da shugabannin jam’iyyar ke yi da kansu. Ya yi zargin cewa wasu gwamnonin jam’iyyar suna son mamaye harkokin PDP ta hanyar amfani da kuɗaɗen gwamnati, abin da ya kira “hanyar lalata jam’iyyar daga ciki.” Ya kuma bayyana cewa idan aka shirya babban taron jam’iyyar ba bisa ka’ida ba, to ba zai halarta ba, sai dai idan an bi doka da tsarin jam’iyya.

    A gefe guda, Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya kira ‘ya’yan jam’iyyar da su hada kai don sake gina PDP a gabannin babban taron jam’iyyar da za a gudanar a Ibadan a watan Nuwamba. Ya ce duk da matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta, PDP na da damar dawo da mulki a 2027 idan shugabanninta suka fifita hadin kai da gaskiya a kan son zuciya.

    Sai dai a yankin Arewa maso Yamma, wasu dattawan PDP sun zargi Ministan Tsaron Ƙasa, Mohammed Bello Matawalle, da tilasta wa magoya bayan PDP komawa jam’iyyar APC ta hanyar amfani da mukamai da dukiya. Sun ce wannan lamari na iya lalata tsarin dimokuraɗiyya da kuma raunana jam’iyyar adawa a shiyyar Arewa maso Yamma, suna roƙon Shugaba Bola Tinubu da ya ja kunnen ministan.

    APC Bello Matawalle Bola Ahmed Tinubu Nyesom Wike PAdp Zamfara
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleƳan Sanda Sun Kama Ƴan Ta’adda 10 a Neja
    Next Article Gwamnonin PDP Sun Zaɓi Tanimu Turaki a Matsayin Ɗan Takararsu a Zaɓen Shugabancin Jam’iyya
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.