Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai sun kama mutum shida da ake zargi da taimaka wa mayaƙan ISWAP wajen gudanar da ayyukansu a Damasak, Jihar Borno.
Rundunar ta ce an kama mutanen ne a ranar 27 ga Yulin 2026, bayan samun bayanan sirri da suka nuna cewa suna taimaka wa ƙungiyar wajen samar da kuɗaɗe ta hanyar saye da sayar da shanu a kasuwannin Gubio, Damasak da Ajuwango.
A cewar sojojin, sun ƙwace makamai, mota da kuma kuɗi Naira 317,950 daga hannun waɗanda ake zargin. Rundunar ta ce waɗannan kayan na daga cikin abubuwan da aka samu yayin kamen.
Rundunar ta ƙara da cewa waɗanda aka kama na ci gaba da fuskantar bincike. Ta kuma jaddada aniyarta ta ci gaba da lalata hanyoyin samar da kuɗaɗe da kayan aiki ga ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.
