Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

      January 15, 2026

      Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

      January 12, 2026

      Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

      January 12, 2026

      Ƴan Bindiga Sun Kashe Soja Da Jam’in NSCDC a Benue

      January 12, 2026

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026
    • Siyasa

      Manyan Jiga-jigan APC 3 a Kogi Sun Mutu

      January 12, 2026

      Ganduje Zai Gana Da Masu Ruwa-da-tsaki Na APC

      January 11, 2026

      Datti Baba-Ahmed Ya Musanta Batun Tsayawa Takarar Shugaban Ƙasa

      January 9, 2026

      Fubara Barazana Ne Ga Demokaraɗiyya – Kakakin Majalisar Rivers

      January 9, 2026

      Kotu Ta Ƙi Bayar da Belin Kwamishinan Kuɗi Na Bauchi

      January 6, 2026
    • Addini

      Kano: Hisbah Ta Karɓi Ƙorafe-Ƙorafe Sama da 12,000 a 2025

      January 2, 2026

      Da Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu

      November 27, 2025

      Zakaran Gwajin Dafi : Hajji 2025 Karkashin Farfesa Saleh Pakistan  

      November 24, 2025

      Hajji Da Shugabanci Nagari Ƙarƙashin Jagorancin Farfesa Pakistan

      November 17, 2025

      Hukumar NAHCON Ta Sanar Da Rage Kudin Aikin Hajjin 2026

      November 10, 2025
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojojin Najeriya Sun Ƙwato lita 290,000 Na Man Fetur a Yankin Neja Delta

      October 21, 2025

      Ƴan Bindiga Sun Ƙwace Wayoyin Ƴan Sanda a Zamfara

      October 2, 2025

      Gwamnan Kano Ya Buƙaci Tinubu Ya Tsige Kwamishinan Ƴan Sandan Jihar

      October 1, 2025

      Will Using a VPN on Phone Helps Protect You from Ransomware?

      January 14, 2021

      Popular New Xbox Game Pass Game Being Review Bombed With “0s”

      January 14, 2021
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Sojoji Sun Yi Juyin Mulki a Guinea-Bissau
    Featured

    Sojoji Sun Yi Juyin Mulki a Guinea-Bissau

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 26, 2025No Comments2 Mins Read

    Wasu jami’an soji a Guinea-Bissau sun bayyana cewa sun karɓi cikakken iko a kasar, a daidai lokacin da ake samun rahotannin kama shugaban ƙasa Umaro Sissoco Embaló. Lamarin ya faru ne jim kaɗan bayan an ji ƙarar harbe-harbe a Bissau, babban birnin ƙasar, inda majiyoyin gwamnati suka tabbatar da cewa an tsare shugaban. Sojojin sun bayyana a gidan talabijin na ƙasa, suka sanar da dakatar da sakamakon zaɓen shugaban ƙasa da aka gudanar a ranar Lahadi, wanda ya kasance cikin takaddama tun kafin kada kuri’u.

    Sojojin sun bayyana cewa za su ci gaba da tafiyar da harkokin ƙasar bayan dakatar da tsarin zabe da suka zargi da rashin gaskiya, inda suka nuna cewa an hana dan takarar adawa shiga zaben. Kasar ta yi shirin sanar da sakamakon a ranar Alhamis, yayin da Embaló da abokin hamayyarsa Fernando Dias suka yi iƙirarin nasara kafin kammala ƙidaya. Janar Denis N’Canha, shugaban sojojin fadar shugaban ƙasa, ya karanta sanarwar da ta ayyana kwace mulki tare da rufe iyakokin Guinea-Bissau gaba ɗaya.

    Kakaki24 ta tattaro cewa Janar N’Canha ya umurci al’ummar kasar da su kwantar da hankali, yayin da rahotanni ke nuna cewa baya ga shugaban ƙasa, an kuma kama hafsan sojojin shugaban ƙasa da wasu ministoci. Wannan mataki ya sake tayar da hankula a yammacin Afirka, yankin da ya sha fuskantar juyin mulki a shekarun baya, ciki har da Mali, Burkina Faso, Nijar da Gabon, lamarin da ke kara tursasa damuwa kan matsayin dimokuradiyya a nahiyar.

    Masu sharhi na ganin cewa rikicin siyasa da rashin yarda kan sakamakon zabe na iya kara dagula lamarin a kasar da ta daɗe tana fama da rikice-rikicen siyasa. Har yanzu babu cikakken bayani game da yanayin da Embaló ke ciki, ko matakin da kungiyoyin yanki irin su ECOWAS za su ɗauka. Ana sa ran karin haske kan lamarin cikin sa’o’i masu zuwa, yayin da kasashen duniya ke kira da a mutunta doka da ‘yancin zabin jama’a.

    Guinea-Bissau
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleTinubu Ya Bayar da Umarnin Gaggauta Ɗaukar Ƴansanda 20,000
    Next Article Majalisar Dattawa Za Ta Tantance Sunayen Sabbin Jakadun Najeriya Da Tinubu Ya Aika
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Shiryawa Ƴan Jaridar Yanar Gizo Horo Na Yini Biyu a Jigawa

    January 15, 2026
    Featured

    Tanka Ta Murƙushe Mutane 5 a Gombe

    January 12, 2026
    Featured

    Babu Siyasa a Binciken Da Ake Yi Wa Malami – EFCC

    January 12, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202542 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202532 Views

    An Gano Motar Ofishin Mataimakin Gwamna Da Aka Sace

    November 12, 202527 Views

    NAFDAC Ta Yi Gargaɗi Kan Wani Kororon Roba Me Matuƙar Haɗari Ga Lafiya

    December 30, 202525 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.