Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Tinubu Ya Bayar da Umarnin Gaggauta Ɗaukar Ƴansanda 20,000
    Featured

    Tinubu Ya Bayar da Umarnin Gaggauta Ɗaukar Ƴansanda 20,000

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 26, 2025No Comments2 Mins Read

    Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, a ranar Laraba, ya ayyana dokar gaggawa kan harkokin tsaro a fadin kasar nan sakamakon karuwar sace-sace, hare-hare da ta’addanci a jihohi daban-daban. Ya bayar da umarnin a dauki karin jami’an ‘yan sanda 20,000 wanda hakan zai kai yawan wadanda ake shirin dauka zuwa 50,000, tare da amincewa da amfani da sansanonin NYSC a matsayin cibiyoyin horaswa na wucin-gadi. Haka kuma ya bukaci jami’an da aka janye daga kula da manyan mutane su samu horaswar gaggawa domin tura su yankunan da ake fama da kalubalen tsaro.

    Tinubu ya kara baiwa rundunar DSS ikon tura masu gadin dazuzzuka domin fatattakar ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga da ke boye a dazuka, tare da umarnin kara daukar ma’aikata domin karfafa wannan yaki. Ya godewa jami’an tsaro kan kubutar da dalibai 24 a Kebbi da masu ibada 38 a Jihar Kwara, tare da bayyana aniyar gwamnati na ci gaba da kokarin ceto daliban da ke tsare a Jihar Neja. Ya kuma bukaci Majalisar Dokoki ta yi garambawul ga dokoki domin baiwa jihohi damar kafa ‘yan sandan jiha idan bukata ta taso.

    A tattaunawarsa da manema labarai, Shugaban ya shawarci hukumomin kananan hukumomi, masallatai da coci-coci su kara tsaurara matakan tsaro, musamman a yankunan da ake fuskantar barazana. Bechi Hausa ta tattaro cewa Tinubu ya kuma jaddada cewa gwamnati ta kirkiro Ma’aikatar Kiwo domin warware rikicin manoma da makiyaya, inda ya bukaci kungiyoyin makiyaya su daina kiwo a fili, su mika makamai ba bisa ka’ida ba, kuma su rungumi tsarin ruga domin zaman lafiya mai dorewa.

    Shugaban kasa ya jajanta wa rundunar soji bisa rasa jarumai ciki har da Birgediya Janar Musa Uba a yayin aikin yaki da ta’addanci. Ya yi kira ga ‘yan kasa kada su firgita, su rika bayar da rahoton abubuwan da ake zargi, tare da hadin kai da hukumomin tsaro. Ya tabbatar da cewa gwamnati na da cikakken kuduri na kare rayuka da dukiyoyi, tabbatar da hadin kai da dawo da zaman lafiya a dukkan bangarorin kasar. “Allah Ya ci gaba da kare Najeriya da kuma kiyaye dakarunmu,” in ji shi.

    Tinubu
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleDa Ɗumi-ɗumi : An Ceto Ɗalibai Mata 24 Da Aka Sace a Kebbi
    Next Article Sojoji Sun Yi Juyin Mulki a Guinea-Bissau
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.