Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, ya ce zai mayar da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Atiku ya bayyana hakan ne yayin wata hira ranar Laraba, inda ya ce gwamnati ta gaza bayyana inda kuɗaɗen da aka samu daga cire tallafin man fetur suka tafi. Ya ce idan aka zaɓe shi, duk wanda ya sace kuɗaɗen zai mayar da su.

Atiku ya ce cire tallafin man fetur zai iya zama abin fahimta ne idan an yi amfani da kuɗaɗen da aka samu wajen ayyukan ci gaba, magance matsalolin tsaro, inganta ilimi da samar da damarmaki ga matasa.

Shugaba Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a jawabin rantsar da shi a ranar 29 ga Mayu 2023. Sai dai Ministan Kuɗi, Taiwo Oyedele, ya ce cire tallafin da sauyin tsarin musayar kuɗi sun samar wa tarayya albarkatun da suka kai naira tiriliyan 15.8 tsakanin Yuni 2023 da Disamba 2025.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version