Dubban mazauna kananan hukumomin Borgu da Agwara a jihar Niger State sun tsere zuwa ƙasar Jamhuriyar Benin bayan sabbin hare-haren ‘yan ta’adda da suka kai farmaki kauyen Konkoso da safiyar Talata 18 ga Fabrairu, 2026. Rahotanni sun ce ‘yan ta’addan sama da 200 ne a kan babura kusan 70 suka sake kai hari, inda suka ƙona gidaje tare da haddasa firgici, lamarin da ya tilasta mazauna tserewa domin tsira da rayukansu.

Majalisar Dattawa ta Najeriya ta yi Allah wadai da kashe mutane sama da 56 tare da sace mata da yara, inda ta bukaci a sake fasalin tsarin tsaron ƙasa baki daya. A lokaci guda, Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa sama da mutum miliyan 3.7 sun rasa muhallansu sakamakon matsalar tsaro, wanda hakan ke kara tsananta rikicin jin kai da tattalin arziki a ƙasar.

Haka kuma, Sufeto Janar na ‘yan sanda, Kayode Egbetokun ya gana da tsofaffin shugabannin rundunar domin neman shawarwari kan yadda za a shawo kan matsalar tsaro. Ya jaddada kudirin rundunar na kara kwarewa da inganta aiki domin rage aikata laifuka, tare da dawo da amincewar jama’a ga rundunar ‘yan sandan Najeriya.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version