Shugaba Tinubu Ya Naɗa Amupitan a Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Koli ta kasa ta amince da nadin Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN) a matsayin sabon shugaban INEC, bayan kammala wa’adin Farfesa Mahmood Yakubu na shekaru 10.

Shugaba Bola Tinubu ya gabatar da sunan Amupitan ga majalisar yayin taron da aka gudanar a fadar shugaban kasa, Abuja. Amupitan, wanda dan jihar Kogi ne kuma lauya mai shekara 58, shi ne mutum na farko daga yankin Arewa ta Tsakiya da aka naɗa wannan mukami.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version