Dakarun rundunar Operation Hadin Kai sun dakile wani hari da mayaƙan ISWAP suka kai a yankin Buratai da ke jihar Borno, bayan wani farmaki na haɗin gwiwa ta sama da ƙasa wanda ya tilasta wa maharan tserewa da asara mai yawa.

A cewar rundunar sojin Najeriya, maharan sun kai hare-hare a wuraren dakaru da ke Dusten Kura da hanyar Chara a ƙaramar hukumar Biu da sanyin safiyar ranar 19 ga Yunin 2026. Sai dai dakarun sojin sun samu bayanan sirri tun da wuri inda suka mayar da martani cikin gaggawa tare da taimakon rundunar sojin sama.

Sojojin sun ce ba a samu asarar rai a ɓangarensu ba, yayin da mayaƙan ISWAP suka yi asarar mutane da kayan aiki masu yawa. Rundunar ta kuma buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin ƙarfafa yaƙi da ta’addanci.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version