Iran ta bayyana cewa za ta yi amfani da dukkan ƙarfin sojinta wajen kare kanta daga duk wani hari da United States da Israel za su kai mata. Sanarwar ta nuna ƙudirin Tehran na mayar da martani idan aka kai mata farmaki.
A wata sanarwa da ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Araghchi, ya fitar, ya ce ya tattauna ta waya da ƙasashen Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, Qatar, Kuwait, Bahrain da Iraƙi. Ya shaida musu cewa Iran a shirye take ta kare kanta da cikakken ƙarfin soji idan buƙatar hakan ta taso.
Araghchi ya kuma tunasar da ƙasashen game da alhakin da ke kansu na hana amfani da yankunansu ko kayayyakinsu ta hanyar da ba ta dace ba. A cewarsa, bai kamata a bai wa Amurka ko Isra’ila damar amfani da ƙasashen wajen ƙaddamar da hari cikin Iran ba.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version