Aƙalla masu haƙar ma’adanai 30 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu 20 ke kwance a asibiti, bayan shaƙar wata iska mai guba da ake zargin carbon monoxide a wani wurin haƙar ma’adanai da ke ƙauyen Zuruk, ƙaramar hukumar Wase a Filato. Lamarin ya faru ne a ranar Talata, kamar yadda mazauna yankin suka tabbatar.
Shaidu sun ce masu haƙar ma’adanai na cikin rami ne lokacin da hayaƙin gubar ya turnuƙe su, lamarin da ya sa da dama ba su samu damar fitowa ba. Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa gubar ta bazu cikin gaggawa, wanda ya haddasa mutuwar mutane da dama, yawancinsu masu shekaru tsakanin 20 zuwa 40. An kuma binne mamatan jim kaɗan bayan faruwar lamarin.
Rahotanni sun nuna cewa an samu nasarar ceto mutum 20 da aka garzaya da su asibiti domin kulawar likitoci, sai dai har yanzu babu cikakken bayani kan halin da suke ciki. Ana sa ran jami’an ƙaramar hukumar Wase za su isa yankin domin gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin, yayin da ake fuskantar ƙalubale wajen ayyukan ceto sakamakon matsalar tsaro.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance ba kan adadin mutanen da suka mutu ko kuma ainihin abin da ya haddasa wannan mummunan hatsari, wanda ya sake jawo hankalin jama’a kan matsalolin tsaro da lafiyar masu haƙar ma’adanai a Najeriya.


