Hukumar Hajj ta Najeriya (NAHCON) ta roki ƙarin kujeru daga Saudi Arabia domin shirye-shiryen Hajji da Umrah na shekarar 2026. Wannan bukata ta fito ne a Abuja ranar Laraba, yayin da NAHCON ke karɓar wata babban tawagar Ma’aikatar Hajj da Umrah ta Saudi, karkashin jagorancin Prof. Ghassan Al-Nuaimi, kafin ziyarar farko ta hukuma ta Ministan Hajj da Umrah zuwa Najeriya.
A yayin ganawar, kwamishinan ayyuka na NAHCON, Prince Anofiu Elegushi, ya bayyana shirye-shiryen Najeriya, ciki har da tsare-tsaren jiragen sama, wuraren kwana a Makkah da Madinah, da kuma gabatar da bayanai kafin isowa. Hukumar ta ja hankalin tawagar Saudi kan kalubalen rage kujeru, iyakance wuraren kwana, matsalolin sufuri da jinkirin bayar da visa na Umrah ga masu shirin yin ibada.
Haka kuma, NAHCON ta bayyana cewa za a gudanar da binciken lafiya ga duk fasinjojin kafin a ba su visa, tare da hana masu matsalolin lafiya tafiya Hajji. An kuma yi tsokaci kan matakan hana tsawaita zama ba bisa ka’ida ba ta hanyar amfani da bayanan biometrics da tsarin bin diddigin fasinjoji. Duk bangarorin biyu sun sake tabbatar da hadin kai don tabbatar da Hajji mai lafiya da nasara ga ‘yan Najeriya a 2026.
