A ranar Talata, shugaban ƙasa Bola Tinubu ya yi tuntube ya fadi kasa a lokacin da yake tafiya a birnin Ankara, babban birnin ƙasar Turkiyya. Lamarin ya faru ne a lokacin da yake tare da takwaransa shugaban ƙasa na Turkiyya, Recep Erdogan.

Kafin faɗuwar, Tinubu ya duba jerin sojoji a wani biki na musamman da aka shirya masa a matsayin tarba. Wannan ya nuna irin martabar da aka ba shi a kasar ta Turkiyya.

Har yanzu ba a samu cikakken bayani kan lafiyar shugaban ba, kuma ƙarin bayani zai biyo baya yayin da ake samun ƙarin rahotanni daga Ankara.

Share.
Leave A Reply

Exit mobile version