Wata babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin tsare tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami SAN, tare da matarsa da ɗansa, Abubakar Abdulaziz Malami, a gidan yarin Kuje bayan sun ƙi amincewa da tuhume-tuhume 16 da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta shigar a kansu.
An gurfanar da su a gaban kotun ne a ranar Talata, inda EFCC ta bayyana cewa tuhume-tuhumen sun shafi safarar kuɗaɗen haramun da kuma mallakar kadarori ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda darajarsu ta haura naira biliyan 8.7.
A cewar hukumar, ana zargin Malami, ɗansa da Hajia Bashir Asabe da amfani da asusun banki da kamfanoni da dama tsawon kusan shekaru goma, domin sarrafa da ɓoye kuɗaɗen da ake zargin sun samo su ta hanyoyin da ba su dace da doka ba.
