Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Matuƙar Atiku Ya Goyawa Obi Baya Tabbas Za Su Kayar Da Tinubu a 2027 – LP
    Featured

    Matuƙar Atiku Ya Goyawa Obi Baya Tabbas Za Su Kayar Da Tinubu a 2027 – LP

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 21, 2025No Comments2 Mins Read

    Jam’iyyar Labour Party (LP) ta sake hura wutar rikici kan haɗin gwiwar ‘yan adawa kafin babban zaɓen 2027, inda ɓangaren jam’iyyar da ke goyon bayan Peter Obi da Gwamnan Abia, Alex Otti, ya bayyana cewa haɗin kai ne kaɗai zai iya kawar da Shugaba Bola Tinubu daga mulki. Kakakin wucin gadin jam’iyyar, Prince Tony Akeni, ya roƙi tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da ya ajiye burin takara ya mara wa Obi baya idan da gaske yana son ceto Najeriya daga halin da take ciki.

    Akeni ya bayyana cewa idan Atiku ya nuna ƙauna ga ƙasar ta hanyar goyon bayan Obi, za a iya samun nasara cikin sauƙi a 2027, yana mai cewa Tinubu “shine shugaban ƙasa mafi sauƙin dokewa a duniya” muddin ‘yan adawa suka haɗa kai. Ya yi gargadin cewa rashin haɗin kai tsakanin manyan ‘yan adawa ne ke ba jam’iyyar APC damar ci gaba da lashe zaɓe.

    Ya kuma soki gwamnatin Tinubu da cewa gwamnati ce mai cika da son kai da yawan sauya sheka, yana mai cewa hakan zai iya haifar da rikici a cikin jam’iyyar mai mulki. A cewarsa, “Tinubu yana ɗauke da abin da zai rushe masa jam’iyya saboda yawan ‘yan siyasar da ke neman matsayi ga cikin kwadayin da ya yi yawa.” Akeni ya yabawa Obi, yana kwatanta shi da tsohon Firayim Ministan Singapore, Lee Kuan Yew, saboda jagoranci cikin hangen nesa da gaskiya.

    Sai dai Atiku ya musanta batun janye wa Obi, yana mai cewa ya fi dacewa a samar da haɗin gwiwar jam’iyyun adawa da za su tantance jagora ta hanyar tattaunawa, ba ta hanyar sadaukar da kai ba. A gefe guda kuma, Mataimakin Shugaban Jam’iyyar LP, Ayo Olorunfemi, ya ce babu wani hatsarin rushewar dimokuraɗiyya ko kafa jam’iyya ɗaya, yana mai cewa ‘yan Najeriya ne suka zabi halin da suke ciki tun daga 2015. Jam’iyyar LP dai har yanzu tana fama da rikicin cikin gida tsakanin ɓangaren Julius Abure da na Obi-Otti yayin da take shirin fafatawa a zaben 2027.

    ADC Atiku Abubakar Labour Party Peter Obi
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleBazan Damu Ba Don Atiku Ya Samu Tikitin Takara a ADC — Obi
    Next Article Za Mu Tsunduma Yajin Aiki Matuƙar Gwamnati Bata Kawo Ƙarshen Matsalolin Malaman Jami’a Ba – Ƙungiyar Ƙwadago
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.