Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Fiye da Janar 500 Aka Tilastawa Barin Aiki Tun Daga lokacin Buhari zuwa Yanzu – Bincike
    Featured

    Fiye da Janar 500 Aka Tilastawa Barin Aiki Tun Daga lokacin Buhari zuwa Yanzu – Bincike

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Rahoton jaridar The Punch ya bayyana cewa sama da manyan hafsoshin soja 500, ciki har da Major-General, Brigadier-General, Rear Admiral da Air Vice Marshal, an tursasa musu yin ritaya daga rundunonin soja tun daga lokacin gwamnatin Muhammadu Buhari zuwa Bola Tinubu, duk da yadda matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a ƙasar. Wannan al’ada ce da ake kira “military tradition”, wadda ke tilasta manyan jami’an da suka fi sabon hafsan hafsoshin soja girma ko suka yi kwas ɗaya da shi su bar aiki domin kiyaye tsarin girmamawa da ladabi a runduna.

    An fara wannan jerin ritaya ne a shekarar 2015, bayan da tsohon shugaban ƙasa Buhari ya nada sabbin hafsoshin soja, inda sama da janar 100 daga rundunar sojojin ƙasa suka bar aiki. Wannan al’ada ta sake maimaituwa a 2021 da kuma lokacin da Tinubu ya hau mulki a 2023, inda karin janar 51 daga rundunar ƙasa, 49 daga rundunar sama, da kuma 17 daga rundunar ruwa suka yi murabus. Sabuwar nadin hafsoshin soja da Tinubu ya yi makon da ya gabata, na iya sake tilasta karin jami’ai 60 yin ritaya idan aka ci gaba da bin wannan tsari.

    Wasu tsofaffin manyan hafsoshi kamar Janar Ishola Williams (rtd.) sun soki wannan tsarin, suna cewa yana kawo cikas ga ci gaban sojoji da tsaro, tare da bayyana shi a matsayin abin da ke kama da tsarin mulkin soja. Sauran tsofaffin hafsoshi sun ce ya kamata gwamnati ta rage yawan janar-janar da ake haɓakawa domin kauce wa irin wannan tarin ritaya, yayin da wasu suka ba da shawarar amfani da gogewarsu a matsayin masu ba da shawara ko hafsoshin ajiya (reserves).

    Sai dai wasu, kamar Janar PJO Bojie (rtd.), sun bayyana wannan al’ada a matsayin abu na yau da kullum a rundunar soja, suna mai cewa yana taimakawa wajen sabunta tsarin aiki da inganta ladabi. Duk da haka, masana harkar tsaro sun jaddada cewa idan aka ci gaba da barin siyasa ta tsoma baki cikin tsarin soja, to za a ci gaba da fuskantar irin wannan matsala ta yawan janar-janar da ake tursasa musu barin aiki duk lokacin da aka nada sabbin hafsoshin runduna.

    Buhari
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamnan Gombe Ya Nuna Alhininsa Kan Mutuwar Mutane 13 Da Hatsarin Mota Ya Rutsa Da Su Daga Gombe Zuwa Kano
    Next Article CBN Ya Fitar Da Dala Biliyan 1.25 Don Shigo Da Man Fetur Duk Da Samuwar Matatar Dangote
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.