Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Saura Ƙiris Mu Daƙile Matsalar Tsaro a Najeriya – Badaru Abubakar
    Featured

    Saura Ƙiris Mu Daƙile Matsalar Tsaro a Najeriya – Badaru Abubakar

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Ministan tsaron Najeriya, Mohammed Badaru Abubakar, ya bayyana cewa gwamnati na gudanar da bincike kan dalilin da ya janyo dawowar hare-haren satar ɗalibai a makarantu da ’yan bindiga suka sake farawa a wasu yankuna na ƙasar. Ya ce duk da cewa akwai raguwar matsalolin tsaro, irin wannan yaki da ’yan ta’adda ba ya ƙarewa cikin sauƙi, domin sukan ɓullo da sababbin dabaru lokaci zuwa lokaci. Badaru ya bayyana cewa akwai wuraren da gwamnati ta sani, amma ba za a iya kai farmaki ba saboda kasancewar su a cikin yankunan da ke cike da jama’a ko kuma daji da ba za a iya harba bam ba.

    A cewarsa, sojojin ƙasar na aiki ba dare ba rana domin murkushe waɗanda ke haddasa wannan sabon tashin hankali. Ministan ya ce gwamnati ba ta taɓa bayyana cewa an kammala kawar da matsalar tsaro gaba ɗaya ba, amma abin da ya fi tayar musu da hankali shi ne dawowar harin da ya ƙaddamar da satar ɗalibai daga makarantunsu. Ya ce ana gudanar da zurfin nazari domin gano ainihin musabbabin komawar wannan barazana da kuma matakan da za a ɗauka don dakile ta gaba ɗaya.

    Badaru ya yi karin bayani kan tsaron makarantu, yana mai cewa gwamnati na da tsari na musamman na kare cibiyoyin ilimi daga hare-haren ’yan bindiga. Ya ce wannan tsari ne ya sa aka samu sauƙi cikin shekaru biyun da suka gabata, inda ba a sami manyan hare-hare da suka shafi ɗalibai ba. Sai dai ministan ya ce ana sake duba tsarin ne domin tabbatar da cewa kura ta kama ne kawai, ba wai barazana ta dawo da ƙarfi ba.

    Ya ƙara da cewa gwamnati za ta karfafa matakai tare da inganta dabarun yaki da ‘yan ta’adda, musamman a yankunan da suka sha fama da matsalar satar ɗalibai. Masu nazari kan tsaro na bayyana cewa dawowar irin wadannan hare-hare na iya shafar burin gwamnati na dawo da kwarin gwiwar iyaye da ɗalibai kan komawa makarantu. Ana sa ran gwamnati za ta sanar da sabbin matakan tsaro cikin makonni masu zuwa domin tabbatar da cewa makarantu sun kasance wurare masu aminci ga yara a fadin Najeriya.

    Najeriya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleJanye Ƴansanda Daga Bawa Manyan Mutane Kariya Zai Jefa Rayuwarmu Cikin Haɗari – Sanatoci
    Next Article Gwamnonin Arewa Sun Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.