Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Bankin Duniya Na Duba Yiwuwar Bawa Najeriya Rancen Dala Biliyan Ɗaya
    Featured

    Bankin Duniya Na Duba Yiwuwar Bawa Najeriya Rancen Dala Biliyan Ɗaya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 2, 2025No Comments2 Mins Read

    Babban Bankin Duniya ya sanya ranar Disamba 16, 2025 a matsayin ranar da zai yanke hukunci kan amincewa da sabon rancen dala biliyan ɗaya ($1bn) da Najeriya ta nema domin tallafawa ci gaban tattalin arziki da samar da ayyukan yi. Sabon rancen, wanda ake kira Nigeria Actions for Investment and Jobs Acceleration, zai haɗa da rabin kuɗin daga Hukumar Ci Gaban Kasa (IDA) da rabin daga Bankin Gyara da Cigaba (IBRD). A cewar bankin, an tsara wannan tallafin ne don ƙarfafa gyare-gyaren tattalin arziki, buɗe damammakin saka jari, da ƙara ayyukan yi a sassan noma, kasuwanci, da fasahar zamani.

    Bankin ya bayyana cewa rancen zai taimaka wajen matsar da Najeriya daga matakin “daidaita tattalin arziki” zuwa “ci gaban da ke amfani ga kowa,” tare da mayar da hankali kan sauƙaƙa hanyoyin kasuwanci da rage tsadar rayuwa. A karkashin shirin, za a inganta damar samun bashi, haɓaka kasuwannin hannayen jari, da aiwatar da dokar Digital Economy and E-Governance Bill 2025, wacce za ta kafa tsarin gwamnati na zamani. Haka kuma za a goyi bayan amfani da yarjejeniyar AfCFTA don rage haraji da sauƙaƙa fitar da kayayyaki zuwa kasashen Afirka.

    Rancen zai kuma taimaka wajen rage hauhawar farashin kayayyaki da inganta samar da abinci ta hanyar ci gaba da noman zamani, musamman a amfanin gona kamar shinkafa, masara da wake. A cewar Bankin Duniya, tsarin zai iya samar da dubban ayyukan yi kai tsaye, musamman ga matasa da ƙananan manoma. Haka kuma, za a ƙara samun ragin haraji da sauƙin shigo da kayan masarufi, abin da zai taimaka wajen rage farashin kayayyaki ga jama’a da ƙarfafa kasuwancin cikin gida.

    Ana sa ran kuɗin za su fito cikin matakai biyu bayan Najeriya ta cika wasu sharuddan manufofi, inda Ma’aikatar Kuɗi tare da Babban Bankin Najeriya (CBN) za su kula da aiwatar da shirin. Wannan sabon rance zai zama ɗaya daga cikin manyan tallafin manufofi da Bankin Duniya ya taba bayarwa ga Najeriya a ‘yan shekarun nan. A halin yanzu, Bankin Duniya ne babban mai ba Najeriya bashi, inda yake da kaso fiye da 41% na bashin ƙasar waje, wanda ya kai dala biliyan 19.39 daga jimillar dala biliyan 46.98 da akebin ƙasar.

    Bankin Duniya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleMun Fara Shirye-shiryen Kai Hari Najeriya – Amurka
    Next Article Har Yanzu Bamu Janye Dakatarwar Shekaru 30 Da Mu Ka Yi Wa El-Rufai Ba – SDP
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.