Tsohon Mataimakin gwamnan jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, ya yi rajista tare da karɓar katin jam’iyyar ADC a mazabarsa ta Gawuna. Wannan mataki na zuwa ne a wani sabon salo na sauya sheƙa a siyasar jihar Kano bayan da ya sanar da ficewarsadagajam’iyyarAPC a ranar Litinin.
Rahotanni sun nuna cewa Gawuna ya gudanar da rajistar ne a hukumance a yankinsa na Gawuna, inda ya samu rakiyar tsohon gwamnan Kano, kuma jagoran Kwankwasiyya Engr. Rabi’u Musa Kwankwaso tare da dimbin magoya bayansa domin shaida wannan mataki. Matakin nasa ya jawo hankalin jama’a, musamman ganin matsayinsa a siyasar Kano.
Ana kallon wannan sauya sheƙa a matsayin wani muhimmin sauyi da zai iya tasiri a siyasar jihar, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen zaɓen shekarar 2027.

