Aƙalla mutum 32 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu sama da 700 suka jikkata sakamakon wata girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 7.1 da ta afku a ƙasar Venezuela. Lamarin ya kuma haddasa lalacewar gine-gine da dama a Caracas, babban birnin ƙasar.
Shaidun gani da ido sun ce an ji girgizar ƙasar har zuwa maƙwabciyar ƙasar Colombia, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito. Tun da farko, Hukumar Gargaɗi Kan Guguwar Tsunami ta Amurka ta yi gargadin yiwuwar afkuwar guguwar a Venezuela da wasu tsibirai da ke yankin.
Hotunan da wakiliyar BBC Vanessa Silva ta ɗauka sun nuna masu aikin ceto suna ci gaba da neman waɗanda suka maƙale ƙarƙashin ɓaraguzan wani ginin bene da ya ruguje a yankin San Bernardino da ke arewacin Caracas. Rahotannin da ba a tabbatar ba sun ce mutum ɗaya ya mutu a yankin.

