Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Gwamnan Kaduna Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan 2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata a Jihar
    Featured

    Gwamnan Kaduna Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan 2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata a Jihar

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 6, 2025Updated:October 6, 2025No Comments2 Mins Read

    Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya amince da fitar da kudi naira biliyan 2.321 domin biyan hakkokin fansho, kudin sallama da tallafin mutuwa ga tsofaffin ma’aikata da iyalan ma’aikatan da suka rasu a fadin jihar.

    Wannan rabo na cikin tsarin fansho na haɗin gwiwa (CPS) da kuma tsohon tsarin biyan fansho (DBS). Gwamnatin Kaduna ta ce ta riga ta biya jimillar Naira Biliyan ₦6.678 a shekarar 2025, tare da jimillar naira biliyan ₦13.5bn cikin shekaru biyu na wannan gwamnati mai ci.

    A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ma’aikatar Yada Labarai ta Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, ya fitar ga manema labarai, ya bayyana cewa kulawa da jin daɗin tsofaffin ma’aikata na daga cikin abubuwan da gwamnati ke ba wa muhimmanci. Ya ce Gwamna Uba Sani ya sha nanata cewa kare mutunci da inganta rayuwar tsofaffin ma’aikata ba kawai wajibi ne na doka ba, har ila yau nauyin ne da gwamnati ke ɗauka da muhimmanci.

    A nasa jawabin, Sakataren Zartarwa na Hukumar Fansho ta Jihar Kaduna, Ibrahim Balarabe, ya ce sabon rukuni na biyan kudi zai amfanar da tsofaffin ma’aikata 661 da iyalan waɗanda suka rasu a matakan gwamnatin jiha da ta kananan hukumomi. Ya bayyana cewa naira biliyan ₦1.736 za a biya wa tsofaffin ma’aikata 511 karkashin tsarin CPS, yayin da naira miliyan ₦585 za a biya wa tsofaffin ma’aikata 315 da iyalan mamata karkashin tsarin DBS.

    Hukumar ta kuma bayyana cewa ga waɗanda ke karkashin tsarin CPS, za a tura kudaden su kai tsaye cikin asusun fansho (Retirement Savings Accounts – RSAs) ɗinsu. Amma ga waɗanda ke karkashin tsarin DBS, za a gayyace su nan gaba domin yin tantancewa kafin biyan kuɗaɗen su.

    A ƙarshe, gwamnatin jihar ta ce wannan mataki ya sake tabbatar da jajircewarta wajen kare rayuwar tsofaffin ma’aikata, tabbatar da hakkokinsu, da kuma ƙarfafa amincewar ma’aikatan jihar da gwamnati.

    Sanata Uba Sani
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleAmbaliyar Ruwa: Har Yanzu Dubban Jama’ar Da Ambaliyar Maiduguri Ta Shafa Basu Samu Matsuguni Ba
    Next Article Tinubu Ya Bawa NAHCON Umarnin Rage Kuɗin Hajjin 2026 Cikin Gaggawa
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.