Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Gwamnatin Kano Ta Ƙudiri Aniyar Aiki Kafaɗa Da Kafaɗa Da Ƙungiyar Ƴan Jaridun Yanar Gizo a Jihar
    Featured

    Gwamnatin Kano Ta Ƙudiri Aniyar Aiki Kafaɗa Da Kafaɗa Da Ƙungiyar Ƴan Jaridun Yanar Gizo a Jihar

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 19, 2025No Comments2 Mins Read

    Gwamnatin Jihar Kano ta kudiri aniyar yin aiki kafada da kafada don bunkasa kafafen yada labarai na internet. Inda ta ayyana su a matsayin hanyar yada labarai mafi sauri a wannan zamani.

    Hakan ya fito ne daga daraktan babban sashen harkokin yada labarai da sadarwa na gwamnati, Alhaji Sanusi Bature Dawakin Tofa, a yayin wani taron horaswa na kwana daya ga ‘yan jaridar intanet, wanda cibiyar Kano Online Media Chapel ta shirya.

    A yayin jawabin sa ga mahalarta taron, Alhaji Sanusi Bature ya nuna goyen baya ga cibiyar tare da tabbatar da cancantar shugabancinta.

    Inda ya yaba da shirya wannan horon na farko da cibiyar ta shirya, yana mai cewa jaridar intanet wata mahimmiyar hanya ce ta sadarwa ga al’umma.

    Daraktan ya sanar da bayar da gudunmawar kudi Naira Miliyan 2 biyan bukatun cibiyar.

    A bangaren kwamishinan harkokin yada labarai na jihar Kano, Comrade Ibrahim Abdullahi Waiya, ya tabbatar da cewa gwamnati tana shirin yin aiki tare da wannan cibiya. Ya ce ma’aikatar harkokin yada labarai za ta ci gaba da tallafawa shirye-shiryen cibiyar tare da tabbatar da sahihancin labarai a kafafen yanar gizo.

    Tun da farko shugaban cibiyar Kano Online Media Chapel, Comrade Abubakar Abdulkadir Dangambo, ya nuna godiya ga halartar jami’an gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki. Ya kuma bayyana cewa tun bayan kafa cibiyar, an mayar da hankali wajen rajistar ‘yan jarida domin tsaftace aikin jarida ta intanet, sannan an bude asusu domin inganta ayyukan cibiyar.

    Dangambo ya bayyana wasu daga cikin kalubalen da cibiyar ke fuskanta, irin su rashin ofishi da rashin isasshen motocin sufuri.

    Duk da wadannan kalubale, shugaban ya tabbatar da kudurin cibiyar na ci gaba da aiki cikin kwarewa, inda ya ce “Zamu ci gaba da watsa sahihan labarai da gaskiya, kuma manufofin mu sun tsaya ne kan gaskiya, rashin nuna bambanci, da hidima ga jama’a.”

    Taron ya samu halartar masu ruwa da tsaki daga bangaren jarida, gwamnati, da kwararru domin nazarin sabbin abubuwa a aikin jarida na internet tare da rawar da fasahar zamani ta AI ke takawa wajen sauya yadda ake gudanar da labarai a zamanin da muke ciki.

    Kano
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kuɓutar Da Ɗaliban Kebbi
    Next Article Kwankwaso Ya Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Gaggauta Gudanar Da Bincike Kan Taɓarɓarewar Tsaro a Ƴan Kwanakin Nan
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.