Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Har Yanzu Mulkin Soja Ake Yi a Najeriya – Femi Falana
    Featured

    Har Yanzu Mulkin Soja Ake Yi a Najeriya – Femi Falana

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 16, 2025No Comments2 Mins Read

    Fitaccen lauya mai kare haƙƙin ɗan adam, Femi Falana (SAN), ya bayyana cewa rikicin da ya faru tsakanin Ministan FCT, Nyesom Wike, da wani jami’in Rundunar Ruwa, Lt. Yerima, ya nuna cewa Najeriya har yanzu tana tafiya ne a yanayin mulkin soja. Ya ce doka ta bai wa minista ikon shiga duk wani fili da ke ƙarƙashin gwamnatin Abuja, sannan hana shi shiga da jami’in soja ya yi, ya saba wa dokar Land Use Act.

    Falana ya ce tsohon hafsan rundunar ruwa, Vice Admiral Awwal Gambo, bai da hurumin tura jami’in soja ya tsare masa fili, domin doka ta haramta amfani da sojoji a rigingimun farar hula. Ya kara da cewa Lt. Yerima bai kamata ya karɓi irin wannan umarni ba, domin umarnin da soji zai bi dole ne ya zama na halal kuma ya shafi aikinsa na soja.

    Ya soki yadda Minista Wike ya zagi jami’in sojan, yana mai cewa hakan ya keta haƙƙinsa na mutunci. Falana ya ce ministan ya yi sakaci, domin ya kamata ya koma ya kai ƙara ko ya sanar da hukumomin soja maimakon yin faɗa da jami’in. Falana ya kuma bayyana cewa martanin wasu manyan hafsoshin soja da suka goyi bayan Lt. Yerima na nuna yadda Najeriya ta kasa cire salon mulkin soja a cikin gwamnati.

    Falana ya ce gwamnati na da alhakin magance irin wannan rikici ta bin doka, musamman ganin yadda jama’a suka nuna goyon baya ga jami’in soja saboda halayen Wike da ake kallon sun yi tsauri. Ya yi kira da gwamnati ta tabbatar da bin doka a rigingimun ƙasa da harkokin gine-gine, tare da nisantar da jami’an tsaro daga shiga rigingimun farar hula domin kiyaye martabar dimokuraɗiyya.

    Femi Falana
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleBama Goyon Bayan Korar Wike Daga PDP – Gwamnan Filato
    Next Article Ƴan Ta’adda 600 Ne Suka Miƙa Wuya Ta Dalilina – Dr Ahmad Gumi
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.