Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Isra’ila Ta Kama Jiragen Ruwan Da Ke Yunƙurin Shigar Da Kayan Agaji Gaza
    Featured

    Isra’ila Ta Kama Jiragen Ruwan Da Ke Yunƙurin Shigar Da Kayan Agaji Gaza

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 3, 2025No Comments2 Mins Read

    Sojojin ruwan Isra’ila sun kama dukkan jerin jiragen ruwa da ke ƙoƙarin kai kayan agaji zuwa Zirin Gaza, tare da tsare daruruwan masu aikin agaji da dama daga ƙasashe daban-daban.

    Lamarin ya faru ne da safiyar Juma’a lokacin da dakarun Isra’ila suka kutsa cikin jirgin Marinette, wanda ke ɗauke da tutar ƙasar Poland. Jirgin, wanda ke da ma’aikata shida, shi ne na ƙarshe cikin jerin jiragen Global Sumud Flotilla da Isra’ila ta kama. A baya, jerin ya ƙunshi jirage 44, waɗanda dukkansu sojojin Isra’ila suka dakatar.

    Kwamitin Ƙasa da Ƙasa na Ƙoƙarin Karya Takunkumin Gaza ya bayyana cewa wasu daga cikin waɗanda aka kama sun fara yajin cin abinci tun daga lokacin da aka tsare su.

    A wata hira ta bidiyo da aka yi a daren Alhamis, shugaban jirgin daga ƙasar Australia, wanda ya bayyana kansa da suna Cameron, ya ce jirgin ya samu matsala da injinsa a farko, wanda ya sa ya ragu a baya. Duk da haka, ya tabbatar da cewa jirgin ya ci gaba da tafiya zuwa Gaza tare da wasu ’yan ƙungiya daga Turkiyya da Oman.

    Bidiyon kai tsaye daga jirgin ya nuna yadda ma’aikatan ke jan jirgin da ƙarfin gwiwa tun ƙarfe 04:00 GMT, a cikin ruwan ƙasa da ƙasa na Tekun Bahar Rum, kusan mil 43 (kilomita 80) daga iyakar ruwan Gaza.

    Ma’aikatar Harkokin Waje ta Isra’ila ta riga ta gargadi jirgin Marinette cewa “ba za a bar shi ya shiga yankin da ake fafatawa ba, kuma ba za a yarda ya karya takunkumin ba.”

    Tun daga ranar Laraba, rundunar ruwa ta Isra’ila ta dakatar da daruruwan jiragen ruwa masu ɗauke da kayan agaji, inda ta kama kusan masu fafutuka 500 daga ƙasashe fiye da 40. Isra’ila ta zarge su da ƙoƙarin karya takunkumin ruwa na doka — zargin da ƙungiyoyin agaji suka ce ya saba dokar ƙasa da ƙasa.

    Daga cikin fitattun mutanen da aka kama akwai Greta Thunberg, tsohuwar magajin garin Barcelona Ada Colau, da Rima Hassan, mamba a Majalisar Tarayyar Turai. Dukkan jiragen da aka kama an tura su zuwa Isra’ila kafin a ci gaba da fitar da ma’aikatansu.

    Isra’ila
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleKotun Tarayya Ta Dakatar Da Rundunar Ƴan Sanda Tilastawa Direbobi Mallakar Lasisin Gilashin Mota Mai Duhu
    Next Article Hukumar NYSC Na Yi Wa Jihar Legas Hidima Ta Kimanin Kuɗi Naira Biliyan 14 Duk Shekara — Darakta Janar
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.