Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Majalisar Dokokin Jihar Benue Ta Amincewa Gwamnan Jihar Ya Ciyo Bashin Naira Biliyan 100
    Featured

    Majalisar Dokokin Jihar Benue Ta Amincewa Gwamnan Jihar Ya Ciyo Bashin Naira Biliyan 100

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 11, 2025No Comments2 Mins Read

    Majalisar Dokokin Jihar Benue ta amince da bukatar da Gwamna Hyacinth Alia ya gabatar mata domin ɗaukar rancen Naira biliyan 100 don aiwatar da manyan ayyukan ci gaban jihar. An amince da bukatar ne a zaman gaggawa da majalisar ta gudanar a ranar Juma’a 10 ga Oktoba, karkashin jagorancin Kakakin Majalisar, Alfred Emberga. A cikin wasikar da aka karanta ga ‘yan majalisar, Gwamna Alia ya bayyana cewa za a yi amfani da kuɗin wajen gyara da samar da kayan aiki a asibitoci 23, gina da gyaran makarantu na kimiyya, kammala ayyukan hanya da gada, gina cibiyoyin koyon sana’o’i da kuma kafa makarantu masu amfani da fasahar zamani a kowane mazabar tarayya a jihar.

    Haka kuma, gwamnatin jihar na shirin amfani da wani ɓangare na rancen wajen gina da samar da kayan aiki ga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Benue (Benue State University of Agriculture, Science and Technology), da ke Ihugh. Bayan tattaunawa, majalisar ta amince da bukatar gwamnan gaba ɗaya tare da jaddada bukatar a yi amfani da kuɗin cikin gaskiya da rikon amana domin bunƙasa ci gaban jihar.

    Sai dai Jam’iyyar PDP ta jihar ta nuna adawa da wannan mataki, tana bayyana shi a matsayin “rashin hankali da ganganci” musamman a wannan lokaci da jama’a ke fama da matsin tattalin arziki. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na jihar, Tim Nyor, ya fitar, PDP ta zargi gwamnati da rashin bayyana gaskiya da cikakken bayani game da rancen. Ta ce wannan lamari na iya jefa jihar cikin wani sabon yanayi na bashin da ba za a iya ɗauka ba.

    PDP ta bukaci majalisar ta sake nazarin matakin da ta dauka tare da taka rawar gani a matsayin mai sa ido kan ayyukan gwamnatin jiha maimakon zama “ƴar amshin shata” ga duk wani shirin gwamnati. Jam’iyyar ta jaddada bukatar yin taka-tsantsan wajen ɗaukar irin waɗannan matakai don kauce wa matsalolin bashi da tasirin tattalin arziki ga jama’ar Benue.

    Benue
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleNAFDAC Ta Haramta Sayar Da Magunguna 101 a Kasuwannin Najeriya
    Next Article Ƴan Boko Haram Sun Kai Hari Sansanin Sojoji a Borno
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.