Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

      July 21, 2026

      Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

      July 21, 2026

      An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

      July 21, 2026

      Guguwa Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi Sun Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane Huɗu a Sakkwato

      July 21, 2026

      Mamakon Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Da Gonaki a Filato

      July 20, 2026
    • Siyasa

      Kotu Ta Yi Watsi da Ƙarar da Tsagin Tanimu Turaki Suka Shigar Kan Rikicin Shugabancin PDP

      July 18, 2026

      Ya Kamata Majalisa Ta Yi Bincike Kan Ingancin Lafiyar Tinubu – ADC

      July 17, 2026

      Gwamna Yusuf Ya Zaɓi Garo a Matsayin Mataimakinsa a Zaɓen 2027

      July 13, 2026

      INEC Ta Ƙara Wa’adin Miƙa Sunayen ‘Yan Takarar Zaɓen 2027

      July 12, 2026

      Sauye-sauyen Gwamnatina Sun Inganta Ayyuka Da Tattalin Arziki a Kaduna – Gwamna Uba Sani 

      July 10, 2026
    • Addini

      An Rufe Birnin Tehran Domin Jana’izar Ayatollah Ali Khamenei

      July 1, 2026

      Kotu Ta Buƙaci a Gabatar Da Litattafan Da Sheikh Abduljabbar Ya Yi Amfani Da Su

      June 29, 2026

      NAHCON Ta Kammala Dawo Da Alhazan Najeriya Daga Saudiyya

      June 23, 2026

      Sarkin Musulmi Ya Buƙaci Hukumomi Su Gaggauta Ɗaukar Matakai Domin Magance Matsalar Tsaro

      June 17, 2026

      Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin ‘Auren Gata’

      June 15, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026

      An Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Sani Yellow a Zamfara

      July 12, 2026

      Matasa a Borno Sun Gudanar Da Zanga-Zanga Kan Rashin Tsaro

      July 12, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » NEMA Ta Karɓi Ƴan Najeriya 147 Da Aka Koro Daga Libya
    Featured

    NEMA Ta Karɓi Ƴan Najeriya 147 Da Aka Koro Daga Libya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 23, 2025No Comments2 Mins Read

    Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi ‘yan Najeriya 147 da suka makale a ƙasar Libya, bayan haɗin gwiwa da ƙungiyar International Organisation for Migration (IOM) da sauran hukumomi. Wadannan ‘yan ƙasa sun iso Najeriya ne a ranar Talata da yamma, ta filin jirgin sama na Murtala Muhammed International Airport, Lagos, cikin jirgin Air Libya mai lambar rajista 5A-BAE.

    A cewar NEMA, cikin waɗanda suka dawo akwai manya 100 (mazaje 32 da mata 68), yara 34 (mazaje 18 da mata 16) da kuma jarirai 13 (mazaje 5 da mata 8). Bayan isowarsu, jami’an hukumar shige da fice (NIS) sun gudanar da rajista da tantance su ta hanyar fasahar kwamfuta, domin tabbatar da sahihancin bayanansu da kuma shirya musu hanyoyin komawa cikin al’umma cikin sauƙi.

    Hukumar ta bayyana cewa an ba wa waɗanda suka dawo taimakon gaggawa kamar abinci da ruwan sha, kula da lafiyar gaggawa, da kuma tallafin sufuri da shawarar kwantar da hankali. Wannan, a cewar NEMA, na cikin tsarin gwamnatin tarayya na tabbatar da dawowar ‘yan ƙasa cikin mutunci da tsaro.

    NEMA ta gode wa hadin kan IOM, Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira da Masu Hijira (NCFRMI) da sauran abokan hulɗa wajen tabbatar da nasarar aikin. Hukumar ta ce za ta ci gaba da tabbatar da cewa kowanne ɗan Najeriya da ke ƙasashen waje cikin mawuyacin hali ya samu damar dawowa gida cikin aminci da kulawa ta ɗan adam.

    Libya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleZan Kare Kaina Bana Buƙatar Lauya – Nnamdi Kanu
    Next Article Najeriya Ta Shigo Da Lita Biliyan 15 Na Fetur Duk Da Samuwar Masana’antar Dangote — NMDPRA
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Ba Kama Gbajabiamila Muka Yi Ba Gayyatarsa Muka Yi – ICPC

    July 21, 2026
    Featured

    Tinubu Ya Naɗa Sabbin Shugabanni Da Mambobi 26 a Hukumomi Da Kwamitocin Gwamnatin Tarayya

    July 21, 2026
    Featured

    An Zargi Likitan El-Rufai Da Bayar da Rahoton Jinya Na Bogi

    July 21, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025150 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202679 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202546 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views

    Dantawaye Ya Zama Sabon Kwamishinan Ƴansanda a Abuja

    October 17, 202533 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.