Rundunar sojin Operation Hadin Kai ta sanar da kashe sama da ‘yan ta’adda 20 daga ƙungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) bayan da suka yi yunƙurin kai hari kan sansanin soji a Goniri da ke jihar Yobe a ranakun 9 da 10 ga Maris.
Kakakin rundunar, Sani Uba, ya ce na’urorin sa ido sun gano ‘yan ta’addan suna tunkaro sansanin daga kauyen Goniri da kuma hanyar Ngamdu da nufin kewaye sojojin. Sai dai sojojin sun mayar da martani da ƙarfi tare da taimakon jiragen yaƙi, lamarin da ya sa maharan suka ja da baya bayan sun yi asara mai yawa.
Sojojin sun kuma kashe wani babban kwamandan ‘yan ta’addan da aka bayyana da suna Abu Yusu, tare da kwato makamai da dama da suka haɗa da bindigogi, bam-bamai da alburusai. Rundunar ta ce yankin na ci gaba da kasancewa ƙarƙashin ikon sojoji yayin da ake gudanar da bincike da sintiri a wuraren da ake zargin wasu daga cikin ‘yan ta’addan suka tsere zuwa.

