Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana aniyarta na kashe kimanin Naira biliyan 1.5 domin gudanar da shirin Auren Gata, wanda aka tanada domin tallafawa matasa masu niyyar yin aure a faɗin jihar.
Kwamandan Hukumar Hisbah ta Kano, Sheikh Aminu Daurawa, ya ce shirin zai haɗa da aurar da mutum 3,000 da suka kunshi amare da ango. Ya bayyana cewa za a bai wa kowane ango Naira dubu 100 domin biyan sadaki, yayin da kowace amarya za ta samu tallafin Naira dubu 100 na jari.
Daurawa ya ƙara da cewa za a horas da amaren sana’o’i domin dogaro da kai, tare da samar musu da kayan daki da kayan abinci don fara rayuwar aure cikin sauƙi. Ya ce nan ba da jimawa ba Gwamna Abba Kabir Yusuf zai sanar da ranar gudanar da ɗaurin auren, kamar yadda BechiHausa ta ruwaito.

