Shugaban Karamar Hukumar Kuje da ke Abuja, Samuel Danjuma Shekwolo, ya bukaci mazauna yankin wadanda ba sa goyon bayan jam’iyyar APC su bar ƙaramar hukumar gabanin zaɓen 2027.
Shekwolo ya bayyana hakan ne a wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, inda ya ce ba zai amince da adawa da APC ko ƙin sake zaɓen Shugaba Bola Tinubu a cikin ƙaramar hukumar ba.
Ya danganta matsayinsa da ayyukan raya ƙasa da ya ce gwamnatin Tinubu da Ministan Abuja, Nyesom Wike, suka aiwatar a Kuje. Ya kuma ce matsayinsa ba abin tattaunawa ba ne, yana mai cewa ko dai mutum yana tare da su ko kuma yana adawa da su.
Kalaman sun jawo martani daga masu amfani da Facebook, inda wasu suka bayyana su a matsayin barazana ga rayuka tare da tambayar inda Hukumar DSS take. Wasu kuma sun ce irin wannan magana ba ta dace da tsarin dimokuraɗiyya ba.
Kalaman shugaban ƙaramar hukumar sun zo ne a daidai lokacin da jam’iyyun siyasa ke ƙara ƙaimi wajen wayar da kan jama’a da gudanar da kamfen a matakin ƙasa da ƙasa gabanin babban zaɓen 2027.

