Majalisar Zartarwa ta Tarayya (FEC) ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta amince da gina filin jirgin sama a garin Gboko na Jihar Binuwai kan kuɗi Naira biliyan 34.5. An amince da aikin ne a wani ɓangare na matakan inganta tsaro da ayyukan ceto.
Ministan Sufurin Jiragen Sama da Raya Sararin Samaniya, Festus Keyamo, ya ce filin jirgin zai sauƙaƙa kai ɗauki ga jami’an tsaro da ma’aikatan agaji zuwa yankunan da ke fama da hare-haren ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane, tare da hanzarta kai taimako ga waɗanda abin ya shafa.
Haka kuma, Ministan Ayyuka, Dave Umahi, ya bayyana cewa FEC ta kuma amince da aiwatar da ayyukan tituna a sassan ƙasar da darajarsu ta kai Naira tiriliyan 3.933. Matakan na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin tarayya na inganta ababen more rayuwa da ƙarfafa tsaro a faɗin Najeriya.

