Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Majalisar Dattawa Na Duba Yiwuwar Baiwa Ƴan Najeriya Damar Riƙe Bindiga
    Featured

    Majalisar Dattawa Na Duba Yiwuwar Baiwa Ƴan Najeriya Damar Riƙe Bindiga

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanNovember 27, 2025No Comments2 Mins Read

    Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kudiri na neman gwamnatin tarayya ta sake duba dokar mallakar bindiga domin bawa ɗaiɗaikun ‘yan kasa masu bin doka damar mallaka, sakamakon ƙarin tabarbarewar tsaro a jihohin Kwara, Kebbi da Neja. Dalilin kudirin ya biyo bayan hare-hare da garkuwa da mutane a makarantu, coci-coci da kauyuka, ciki har da harin da aka kai cocin CAC a Eruku ranar 18 ga Nuwamba, inda aka kashe mutane biyu aka yi garkuwa da 38 waɗanda daga bisani aka sako su. Sanatoci da dama sun jaddada buƙatar ɗaukar matakin gaggawa don dakile ta’addanci, fashi da makami, da yawaitar sace ɗalibai da ke tilasta rufe makarantu da dubban yara ke karatu.

    A yayin muhawara, sanatoci sun yaba wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa soke tafiyarsa zuwa kasashen waje don jagorantar martanin tsaro wanda ya taimaka wajen kubutar da waɗanda aka yi garkuwa da su a Kwara da kuma ‘yan matan makaranta 24 na Kebbi. Sai dai wasu sanatocin sun bukaci bayyana wanda ya bayar da umarnin janye sojoji kafin sace ɗalibai a Maga, inda suka bayyana hakan a matsayin alamar matsalar cikin gida a hukumomin tsaro. Wasu kuma sun nuna damuwa kan kisan Brig-Gen Musa Uba da suka ce ya kara nuna tabarbarewar amincewa da dabarun tsaron kasa.

    Shugaban marasa rinjaye da wasu sanatoci sun yi kira da a binciki yiwuwar masu fallasa tsari a cikin jami’an tsaro tare da tabbatar da sake fasalin tsarin tsaro cikin gaggawa domin karya karfin ‘yan ta’adda. Sanata Barau Jibrin ya jaddada cewa lamarin tsaro ba na gwamnatin tarayya kaɗai ba ne, inda ya bukaci gwamnatocin jihohi, kamfanoni, da al’umma su mara baya domin saurin shawo kan kalubalen tsaro. Ya kuma nemi jihohi su zuba jari a kayan sa-ido da hanyoyin tattara bayanan sirri domin taimakawa rundunonin tsaro su fi saurin daukar mataki.

    Majalisar Dattawa ta kuma kada kuri’ar bukatar a yi gyara ga dokar bindiga domin ta dace da kalubalen tsaro na yanzu, kamar yadda kasashe sama da 175 ke ba da damar mallakar bindiga ga ‘yan kasa masu bin doka. Sanatoci sun ce lokaci yana kurewa, kuma dole ne gwamnati ta dauki tsattsauran mataki kan ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da miyagu da ke addabar al’umma. Sun ce rayuka na salwanta kuma wannan ba lokacin wasa ko nuna siyasa ba ne, domin matsalar na bukatar dabaru, kwarewa, da himma gaba ɗaya domin mayar da kasar kan turbar zaman lafiya.

    Majalisar Dattawa
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleDa Ɗumi-ɗumi : Sheikh Dahiru Bauchi Ya rasu
    Next Article Sama Da Mutane Miliyan Ɗaya Sun Kammala Rijistar Katin Zaɓe – INEC
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.