Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    • Shafin Farko
    • Labarai

      Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

      September 4, 2026

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

      September 3, 2026

      Gwamnatin Kano ta fitar da iyakoki tsakanin Jam’iar Bayero da alummar Rimin Zakara bayan kammala biyan diyya

      September 3, 2026

      Ƙungiyar Miyetti Allah Ta Buƙaci Tinubu Ya Sa a Saki Shugabanta

      September 3, 2026
    • Siyasa

      A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

      September 4, 2026

      Ɗan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a NDC Na Shirin Komawa APC

      September 2, 2026

      Ƴan Siyasa Ne Matsalar Najeriya – Peter Obi

      August 31, 2026

      Bai kamata Tinubu ya bar Najeriya a dai dai lokacin da matsaloli ke addabar ƙasarsa ba – Atiku

      August 31, 2026

      Atiku Ya Yi Alkawarin Sake Buɗe Iyakokin Najeriya Idan Ya Lashe Zaɓen 2027

      August 28, 2026
    • Addini

      Shugaban Asibitin Kwararru na Best Choice, Na Taya Gwamnan Kano Da Al’umma Bikin Murnar Maulidi Annabi SAW

      September 2, 2026

      Hajj 2027 : Kano ta kammala sayar da kujeru 3,050 da aka ware wa jihar

      August 31, 2026

      Gwamnatin Kano ta bayar da hutu domin bikin Takutaha

      August 26, 2026

      Wasu Malamai Daga Arewacin Najeriya Sun Goyi Bayan Tazarcen Tinubu

      August 23, 2026

      Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata a matsayin ranar hutun Maulidi

      August 21, 2026
    • Nishadi

      Oculus Founder Makes a VR Headset That Can Literally Kill You

      January 13, 2021
      85

      Braun Series 7 Electric Shaver Review: Quality at a Good Price

      January 13, 2021
      85

      Google Pixel 7, iPhone 14 Compared: Check Out 5 Major Differences

      January 13, 2021

      Why Apple Should Skip The MacBook Pro Launch

      January 12, 2021

      Apollo G2J Showcases Electric Sports Car

      January 12, 2021
    • Tsaro

      Ƴanbindiga Sun Sace Shugaban Jam’iyyar ’iyyar APC Na Ƙaramar Hukumar Rogo

      September 1, 2026

      Amurka Za Ta Janye Sojoji Kusan 200 Daga Najeriya

      August 28, 2026

      Sojoji Sun Kama Ƴan Ƙasashen Waje Da Ake Zargin Suna da Hannu a Matsalar Tsaron Najeriya – Bwala

      July 18, 2026

      ‘Yan Sanda Sun Fara Kwato Makaman Da Ke Hannun Jama’a Ba Bisa Ka’ida Ba – IGP Disu 

      July 17, 2026

      Sojoji Sun Gano Ƴan Ƙasashen Waje Uku Cikin Mayaƙan ISWAP a Borno

      July 13, 2026
    BECHI HAUSA NEWSBECHI HAUSA NEWS
    Home » Ministan Kuɗi Wale Edun Ya Tafi Birtaniya Don Neman Lafiya
    Featured

    Ministan Kuɗi Wale Edun Ya Tafi Birtaniya Don Neman Lafiya

    Abbass AbdurrahmanBy Abbass AbdurrahmanOctober 15, 2025No Comments2 Mins Read

    Ministan Kuɗi kuma Ministan Tsare-tsaren Tattalin Arziki na Ƙasa, Mista Wale Edun, ya tafi ƙasar Birtaniya domin samun kulawar likitoci, bayan ya yi rashin lafiya a kwanakin baya. Majiyoyi da dama daga fadar gwamnati sun tabbatar da hakan da safiyar Talata, inda suka bayyana cewa ministan ya bar Abuja zuwa Legas da daddare, daga nan kuma ya wuce Landan ta jirgin British Airways.

    Tun a ranar Lahadi, wasu jami’an gwamnati sun bayyana cewa Edun na karɓar magani a gidansa a Abuja karkashin kulawar likitocin Najeriya, suna mai ƙaryata jita-jitar cewa ya kamu da ciwon bugun jini. Sai dai daga baya, likitoci sun ba da shawarar a kai shi ƙasashen waje don ci gaba da jinya, wanda aka aiwatar a yanzu.

    Wani babban jami’in gwamnati ya tabbatar da cewa Edun na fama da rashin lafiya mai ɗan tsanani amma ba ciwon da zai hana shi aiki gaba ɗaya ba. Haka kuma, mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin labarai, Bayo Onanuga, ya tabbatar da cewa Edun ba zai iya halartar taron shekara-shekara na Bankin Duniya da IMF da ke Washington, D.C. ba. Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Olayemi Cardoso, ne zai jagoranci tawagar ƙasar.

    Edun, wanda aka naɗa a watan Agustan 2023, ya taka muhimmiyar rawa wajen aiwatar da manufofin tattalin arzikin gwamnatin Tinubu, ciki har da cire tallafin mai da daidaita farashin musayar kuɗi. Har yanzu Ma’aikatar Kuɗi ba ta fitar da wata sanarwa ta hukuma kan halin da ministan ke ciki ba.

    Birtaniya
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Previous ArticleGwamna Mbah Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa APC
    Next Article Za a Samu Ƙarancin Wutar Lantarki Na Tsawon Kwanaki 10 a Gombe – TCN
    Abbass Abdurrahman
    • Website

    Related Posts

    Featured

    Najeriya Ta Musanta Zargin Goyon Bayan Yunƙurin Juyin Mulki a Nijar

    September 4, 2026
    Featured

    A shirye nake na mutu domin kare ƙuri’ata – Peter Obi

    September 4, 2026
    Featured

    Sarkin Gumel Alhaji Ahmed Muhammad Sani Ya Rasu 

    September 3, 2026
    Add A Comment
    Leave A Reply Cancel Reply

    SABBIN LABARAI

    Ba Don Gudunmawar Masu Yiwa Ƙasa Hidima Ba Da Jihohi Dayawa Basu Kai Yadda Suke a Yanzu Ba – Minista

    December 8, 2025229 Views

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai a NDC : Ƴan Takara Sun Kai Ƙara Kan Zaɓen Fidda-gwani a Kano

    June 30, 202680 Views

    Gwamnatin Kano Ta Dakatar da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

    October 1, 202551 Views

    Gwamnatin Kano Ta Raba Filaye Ga Masu Taimakawa Gwamna Sama da 2,500

    August 1, 202644 Views

    Kotu Ta Yankewa Tsohon Firayim Ministan Mali Hukuncin Zaman Gidan Yari Sakamakon Rubutu a Shafin Sada Zumunta

    October 27, 202541 Views
    Stay In Touch
    • Facebook
    • TikTok
    • WhatsApp
    • Twitter
    • Instagram
    • Telegram
    © 2026 Bechi Hausa News. Developed by: ENGRMKS & CO.
    • Shafin Farko
    • Game da Mu
    • Ƙarin Bayani
    • Manufar Sirri
    • Ka’idoji da Sharudda
    • Tuntuɓe Mu

    Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.