Rundunar sojin Najeriya ta sanar da ceto mutum biyar da aka sace a jihar Kogi, bayan da masu garkuwa da su suka tsere sakamakon matsin lambar hare-haren da sojoji ke ci gaba da kai wa maboyarsu.
Lamarin ya faru ne ranar 17 ga Yunin 2026 yayin wani samamen tsaro daga sansanin sojin Oshokoshoko zuwa hanyar Adankolo, inda sojojin suka gano waɗanda aka sace bayan maharan sun yi watsi da su suna gudun tsira.
Bayan ceto su, an kwashe mutanen zuwa wurin da ke da tsaro tare da kai su cibiyar lafiya ta soji domin kula da lafiyarsu. Rundunar ta ce tana ci gaba da tattara bayanan sirri daga hannun waɗanda aka ceto domin gano sauran ‘yan ta’addar da ke aiki a yankin.

