Mutum 11 da suka haɗa da mata biyar da yara shida, waɗanda aka bayyana a matsayin ‘yan uwan mayakan Boko Haram, sun miƙa wuya ga dakarun Operation HADIN KAI a Banki, ƙaramar hukumar Bama ta Jihar Borno.
Rahotanni sun ce mutanen sun fito ne daga ƙauyukan Chongolo da Ladantar, inda aka ce sun tsere daga maɓoyar ‘yan ta’adda domin neman mafaka. Bayan tantance su, sojoji sun miƙa su zuwa sansanin ‘yan gudun hijira na Bama domin ci gaba da kula da su da kuma shirin gyaran hali.
Majiyoyin soji sun bayyana cewa wannan na daga cikin ci gaba da miƙa wuya da ake samu sakamakon matsin lambar da Operation HADIN KAI ke ci gaba da yi wa ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya a Arewa maso Gabas. BechiHausa ta ruwaito cewa jami’an tsaro sun ce duk da yanayin tsaro ya dan lafa, sojoji na ci gaba da kasancewa cikin shiri domin dakile duk wata barazana.

